Gwamnatin Kano ta dakatar da daukacin makarantun kudi na Jihar da nufin sake nazari a kan yadda ake gudanar da su, a cewarta.
Matakin dai ya biyo bayan kururuwar da al’umma ta yi bayan gano gawar Hanifa Abubakar, wata daliba da ake zargin shugaban makarantar da take ya sace, ya kuma kashe ta.
A shirin Najeriya a Yau za mu ji hikimar yin hakan da ma yadda hakan zai shafi ilimi a Jihar.